Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
Babban Hafsan Sojin kasa Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya bayyana fatansa na cewa, nan ba da jimawa ba za a kawar da kungiyar Lakurawa, ta hanyar ƙarfafa hadin gwiwa da kasashen da ke makwabtaka da Nijeriya.
Oluyede ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan ganawarsa da shugaban kasa, Bola Tinubu a Abuja.
Da ya ke jawabi a ziyarar tasa, Laftanar-Gen. Oluyede ya jaddada ƙudirinsa na inganta yanayin tsaro a Najeriya, in da ya yi alƙawarin samar da sabuwar hanyar magance matsalar rashin tsaro.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta yi martani kan rahoton Amnesty.
Sojojin Najeriya sun yi raga-raga da sansanonin ƴan bindiga a jihar Taraba.
Babban jami’in ya kuma bayar da bayanai kan ziyarar da ya kai a sansanonin sojoji a Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.
Ya bayyana cewa, ganawarsa da dakarun sojojin ta jaddada muhimmancin kawo ƙarshen rashin tsaro a faɗin Najeriya.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Peter Obi ya gode wa Ƴansanda kan janye gayyatar da su ka yi wa Sarki Sunusi.
-
SERAP ta buƙaci Tinubu da ya ƙi amincewa da bashin dala biliyan $1.08 da Bankin Duniya ya amince da shi kwanan nan.
-
Wani mayaudari ya damfari Bobrisky Dalar Amurka 990.
-
Rasuwar Sheikh Idris: mun “fawwala komai ga Allah maɗaukakin Sarki”- Gwamnan jihar Bauchi.
-
Kotun koli ta soke hukuncin da ya bai wa tsagin da ke adawa da Obi a jam’iyyar LP nasara