Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Muhammad yayi kira ga al’umar jihar da ɗaukacin ƴan Najeriya da su ƙada ƙuri’un su ga jam’iyyar PDP a zaɓukan dake tafe don cigaba da sharɓar romon dimokraɗiyya.
Yayi wannan kira ne a ƙaramar hukumar Gamawa yayin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓe karo na biyu inda ya jaddada aniyar gwamnatin sa za ta cigaba da samar da ayyukan ɗaga darajar jiha ta hanya bunƙasa tattalin arzikin ta.
Ya yabawa masu riƙe da sarautun gargajiya kan rawar da suke takawa wajen inganta zaman lafiya da ciyar da al’uma gaba.
A jawaban su daban daban Hakiman Udubo da Gamawa yabawa salon mulkin gwamnatin Sanata Bala Muhammad suka yi kan samar da manyan ayyuka a yankin ciki har da kammala fitacciyar hanyar Bulkachuwa zuwa Udubo da gwamnatin da ta shuɗe tayi watsi da su.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Idan Na Zama Dan Majalisa Zan Samar Da Shirin Wayar Da Kan Mutane Don Su Gane Yadda Ake Shugabanci- Jarumin Wannan Kwaikwayo Dadi.
-
Gwamna Bala ya sha alwashin inganta tsaro, yaƙi da talauci, yayi yaƙin neman zaɓe a Itas
-
Ƴan siyasa ku guji amfani da mimbarin Wa’azi domin biyan bukatar ku – Abdulkarim Tilde
-
Kungiyar Matasa masu hankoron ganin Gwamna Bala ya dawo a 2023 ta gudanar da babban taron shugabannin ta a jihar Bauchi
-
Bauchi: Ɗan Takarar Majalisa A PDP Ya Yi Umarnin Al’ummar Alƙaleri Da Kirfi Su Zaɓi APC.