Daga Suleman Ibrahim Moddibo
Mutum 577 sun warke daga Korona cikin sa’o’i 24 wato a ranar Litinin 17 ga watan Junairun shekarar 2022 a Najeriya, wanda kuma cutar ta sake kama mutum 249 da suka fito da daga wasu jihohin Najeriya guda 14 har da birnin tarayya Abuja 15.
Hukumar da ke yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa ta Najeriya NCDC ce, ta sanar da hakan a shafi na Twitter inda ta ce jihar Lagos ce aka fi kamuwa da mutum 59 sai jihar Adamawa mutum 46 inda jihar Imo ta smau mutum 37 da suka kamu da cutar.
249 new cases of #COVID19Nigeria;
Lagos-59
Adamawa-46
Imo-37
FCT-30
Kwara-14
Rivers-13
Kaduna-10
Taraba-9
Cross River-8
Bauchi-7
Niger-5
Delta-4
Ogun-4
Nasarawa-2
Kano-1251,178 confirmed
224,629 discharged
3,110 deaths #TakeResponsibility pic.twitter.com/UAm1QsAJ5K— NCDC (@NCDCgov) January 17, 2022
A babban birnin tarayyar Najeriya Abuja mutum 30 aka samu a ranar Litinin sai jihar Kwara mutum 14 inda jihar Rivers aka samu mutum 13, yayin da jihar Kaduna ke da mutum 10.
Sauran jihohin dai sune Taraba 9 Cross River8 da jihar Bauchi mai mutum 7 ita kuwa jihar Niger mutum 5 ne suka kamu jihar Delta da Ogun huɗu-huɗu Nasarawa na da mutum 2 Jihar Kano ce ta ƙarshe da mutum guda ya kamu a ranar.
Najeriya: Korona Ta Kashe Mutum 8 Ta Kuma Kama 301.
Mutum 50 Sun Kamu Da Korona A Jihar Gombe.
Har Yanzu Jihar Kaduna Na Fama Da Cutar Shan Inna.
Alƙaluman da hukumar ta fita sun yi nuni da mutum 7 ne suka rasa rayukansu yayin da wanda hakan ya kai ga baki ɗaya waɗanda suka mutum a Najeriya ya kai 3,110.
Zuwa yanzu an tabbatar da cutar ta kama mutum 251,178 tun daga bullar ta yayin da kuma mutum 224,629 suka warke daga Korona a cewar sanarwar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Bauchi: Gwamnan Jihar Bala Muhammad Ya Gina Katafaren Asibiti A Garin Dambam.
-
Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar Da Shirin Rage Haihuwa A Najeriya.
-
Shin Da Gaske Ne Buhari Ya Yi Kyautar Mota Ga Wani Bawan Allah?
-
Jigawa : Hisbah ta ƙwace kwalaben giya tare da kama karuwai 92.
-
Najeriya: Korona Ta Kashe Mutum 8 Ta Kuma Kama 301.