Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta cafke wani matashi yana sojan-gona da hukumar.
KAROTA, ta sanar da kama hakan ne cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa, inda ta ce, ta cafke matashin ne dai-dai lokacin da yake tsaka da tare motoci akan titi sha biyu na daran ranar Litinin.
“Matashin mai suna Lukman Abdullahi mai shekaru 27 mazaunin unguwar Sabon Gari bayan kama shi ya bayyana cewa shi ɗan Maiduguri ne,” in ji sanarwar.
Shugaban Hukamar Karota Na Jihar Kano Ya Kasa Bayyana A Gaban Kotu.
Gwamnatin Kano Ta Yiwa Sheikh Qaribullahi Kabara Kyautar Fili.
Nabilusi ya kuma ce, matashin yana amfani da kayan ne saboda jama’a su fahimci shi ma’aikacin hukumar ne.
“hukumar ta jima da samun rahoton yadda matashin yake amfani da yawunta wajen cusgunawa al’umma, wanda sai a wannan karon dubunsa ta cika.”
shugaban Hukumar ta KAROTA Baffa Babba Ɗan’agundi ya shawarci al’umma da su cigaba da kai rahoton duk wani jami’in da suka ga yana karɓar cin-hanci domin ya fuskanci tuhuma, cewar sanarwar.
Nabulusi ya kara da cewa idan suka kammala binke akansa zasu miƙa shi hannun jami’an Yansanda domin faɗaɗa bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar tuhuma.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Tinubu ya rantsar da sabon Sakataren Gwamnatinsa Akume
-
Kungiyar Ƴan Jarida ta ƙasa NUJ za ta bi sa sahun Kungiyar Kwadago NLC don Tsunduma yajin aiki kan cire tallafin Mai
-
Tsohuwar Ministar mata Pauline Tallen ta shiga hannun EFCC kan zargin Almundahana
-
Kotu Ta Bawa Ƴan Sanda Umarnin Kama Sheikh Idris Dutsen Tanshi Bisa Rainata.
-
Bayan Shan Rantsuwa Tinibu Ya Ce Daga Yanzu Gwamnatinsa Za Ta Soke Tallafin Man Fetur.