Daga Fa`izu Muhammad Magaji
Wata kotun addinin Musulunci mai lamba biyu da ke zama a Tashar Babiye a birnin Bauchi, ta daure wani matashi Abubakar Sadik, mazaunin A A Waziri da ke Bauchi, bayan samun sa da laifin shiga gidan tsohon gwaman jihar Bauchi Barrister Abdullahi Abubakar M.A, ba tare da izini ba, har ta kai ga ya yi sata a gidan.
Matashin wanda rundunar yan sandan jihar Bauchi ta gurfanar da shi a gaban kotu an zarge shine da shiga gidan tsohon gwamanan ba da izini ba, inda kuma ya sace na`urar sanyaya daki, zargin matshin ya amsa aikatawa a gaban kotu.
Bayan amsa laifinsa Alkalin kotun mai shari’a Barrister Muktar Adamu Bello Dambam, ya yankewa matashin hukuncin daurin watanni 15 gidan gyaran hali, ko kuma biyan naira dubu Ashirin da Biyar, ya kuma ba da umurni, mayar da kayan da matshin ya sata ga mai su nan take.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Amaryar Ta Rasa Idonta Daya Ne Ana Tsaka Da Bikinta Sai Dai Duk Da Haka An Daura Mata Aure Da Angonta.
-
Zargin Taimakawa Ta’addanci: SSS Sun Mamaye Hedikwatar Babban Bankin Najeriya.
-
Gwamna Bala ya sha alwashin inganta tsaro, yaƙi da talauci, yayi yaƙin neman zaɓe a Itas
-
Ciyar Da Jihar Bauchi Gaba Ne Muradin Mu, Ku Sake Ba Mu Dama – Saƙon Gwamna Bala Ga Al’umar Udubo
-
Ƴan siyasa ku guji amfani da mimbarin Wa’azi domin biyan bukatar ku – Abdulkarim Tilde