Babbar kotun Tarayya da ke zaman ta a Gyaɗi-gyaɗi a Kano ta umarci Gwamnatin jihar ta biya ƴan Kassuwar da ke da shaguna a filin Masallacin Idi da ke Ƙofar Mata Naira Biliyan 30 bisa rushe musu shaguna ba bisa ƙa’id ba.
Freedom Radio ta rawaito, a yayin zartar da hukuncin Mai Shari’a Simon Ameboda ya ce bin dare tare da rushe shagunan talakawa haramtaccen aiki ne mai cike da tsantsar zalunci da ƙeta, don haka lallai Gwamnati ta biya masu shagunan.
Haka kuma kotun ta hana Gwamnatin Kano shiga cikin filayen da yin tasirifi da shagunan balle bayar da su ga wani.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja
-
Fasinjojin wata mota huɗu sun riga mu gidan gaskiya wasu kuma sun jikkata a jihar Borno.
-
Yan Sandan Jihar Kaduna sun kama Ƴan Daba bisa zargin kai wa masu ibadar Sallar Tahajjud hari.
-
Kotun Ƙoli ta raba gardama kan rikicin Sakataren jam’iyyar PDP na tarayyar Najeriya.