Mayakan jihadi sun kai hari sansanin soji da wani yankin Borno tare da kashe sojoji 9, da ‘yan sanda biyu da kuma farar-hula, kamar yada majiyoyin tsaro da mazauna yanki suka tabbatar.
Mayakan IS sun farwa garin Malam Fatori, a ranakun daren Juma’a da kuma safiyar Asabar, a cewar majiyoyin.
A cewar bayanan da aka fitar, an tafka asara sosai a harin.
Harin na farko, a kusa da iyakar Najeriya da Nijar anyi ɓarin wuta sosai tsakanin sojoji da mayakan, a cewar Buji Garwa.
A watan Maris da ya gabata ne, dubban mutane da rikicin Boko Haram ya tilastawa tserewa zuwa Nijar, suka dawo yankunansu a Malam Fatori.
Mun dauko wannan labarin a shafin kai tsaye na BBC Hausa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Rundunar Ƴan Sandan Jihar Kano Ta Gargadi Mazauna Jihar Kan Atisayen Harbin Bindiga A Kalebawa.
-
Ba Zamu Lamunci Daba Da Shaye-Shaye A Unguwarmu Ba- Al`Ummar Dala.
-
Ayyukan Laifin Da Aka Aikata A Kano Cikin Shekarar 2022 Sun Ragu Fiye Da 2021- Ƴan Sanda.
-
Jami’an Tsaro Sun Hallaka Ƴan Bidinga Tare Da Ragargaza Maɓoyarsu.
-
TSARO: Gwamnatin Buni ta na ci gaba da bai wa jami’an tsaro cikakken goyon baya don tunkarar matsalolin tsaro a Yobe