Daga: Suleman Ibrahim Moddibo
Sabbin alƙaluman da hukumar da ke yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta fitar a jiya Lahadi 16 ga watan Junairun shekarar 2022 sun ce, sabbin mutum 301 ne suka ƙara kamuwa da cutar Korona a ƙasar.
Jihohin da waɗanda suka kamun suka fito sun haɗa da jihar Lagos mai mutum 175 wanda ita ce kan gaba, sai mai biye mata jihar Ondo da mutum 42 jihar Osun na da 23 jihar Rivers mutam 21.
Sauran sune jihar Nasarawa mutum 16 sai Oyo inda mutum 8 suka kamu jihar Gombe 7 Kaduna 7 babban birnin tarayyar Najeriya Abuja na da mutum 1 jihar Kano 1.
Sanarwar da NCDC ta wallafa a shafin ta na Twitter ta yi nuni da cewa mutum 8 ne suka rasa rayukansu ranar inda zuwa yanzu aka sallami 224,052 da suka warke daga cutar.
301 new cases of COVID19Nigeria;
Lagos-175
Ondo-42
Osun-23
Rivers-21
Nasarawa-16
Oyo-8
Gombe-7
Kaduna-7
FCT-1
Kano-1250,929 confirmed
224,052 discharged
3,103 deaths pic.twitter.com/pIiyaxco5Z— NCDC (@NCDCgov) January 16, 2022
Mutane 250,929 hukamar ta tabbatar da sun kamu da cutar a Najeriya yayin da mutum 3,103 suka mutu sanadiyar cutar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Kano: Sinadari Mai Guda Ya Jawo An Kwantar Da Sama Da Mutum 200 A Asibiti.
-
Bauchi: Gwamnan Jihar Bala Muhammad Ya Gina Katafaren Asibiti A Garin Dambam.
-
Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar Da Shirin Rage Haihuwa A Najeriya.
-
Shin Da Gaske Ne Buhari Ya Yi Kyautar Mota Ga Wani Bawan Allah?
-
Jigawa : Hisbah ta ƙwace kwalaben giya tare da kama karuwai 92.