Kungiyar Dattawan Arewa ta yi watsi da matsayar da gwamnonin yankin kudu suka cimma, na cewa wajibi ne shugaban kasa ya fito daga yankin kudu a zaben shekara ta 2023.
Kungiyar ta ce ba wani yanki da za’a ce tilas shi ne zai samar da shugabancin kasa a tsarin dimokaradiyya, domin kuwa mukami ne da ake zaben kowane mutum, kuma daga ko wane yanki ya fito.
A cewar kungiyar, kujerar shugaban kasa mukami ne da ake samu ta hanyar dimokaradiyya, ba wai tsarin karba-karba ba.
Kungiyar tana mai da martani ne akan matsayar da gwamnonin kudancin Najeriya suka cimma a wani taro da suka yi a birnin Ikko a ranar Litinin, inda suka ce tilas a baiwa yankin na kudu damar fitar da shugaban kasa, bayan karewar wa’adin mulkin shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2023.
VOA Hausa tace “Kungiyar ta amince abi mataki na bai daya cewa, a rika mulkin karba-karba tsakanin kudanci da arewacin Najeriya, ta kuma amince cewa, shugaban Najeriya na gaba, ya fito daga yankin kudanci.” In ji sanarwar da kungiyar ta fitar a karshen taron na Legas, mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar, gwamnan jihar Ondo, Arakunrin Oluwarotimi Odunayo Akeredolu.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Sama Da Mutane Dubu 10 Ne ke Cin Moriyar Motocin Da Gwamna Bala Ya Rabawa Direbobi Da Masu Aikin Mota,-RTEAN.
-
Atiku Ya Gana Da Sanatocin Jam’iyyar PDP.
-
Ɗan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa Na Jam`Iyyar APGA Ya Bukaci Sarkin Muslmi, Shugaban Kiristoci Su Umarci Yan Najeriya Su Yi Azumi.
-
An Juya Min Zance Kan Batun Wakiltar Musulunci A Gwamnatin Tinubu -Kashim Shatima
-
Sadiq Wali Ne Ɗan Takarar Gwamna Na Jam’iyar PDP A Kano,-INEC.