June 8, 2023

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Yan Sanda A Kano Na Zargin Sabon Zaɓaɓɓen Ɗan Majalisar Tarayyar Najeriya Da Mallakar Bindiga Ba Bisa Ƙa’ida Ba.

Page Visited: 141
0 0
Read Time:41 Second

Daga Suleman Ibrahim Modibbo

Rundunar ƴan Sandan jihar Kano, da ke Arewacin Najeriya, ta ce, ta gayyaci tare da tsare zaɓaɓɓen ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙaramar Dala Aliyu Sani Madaki a ranar Laraba ɗaya ga watan Maris.

Mai magana da yawun rundunar Ƴan Sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya aikewa manema labarai.

A cewar yan sanda ana zargin Madaki da mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba “a yanzu haka yana sashin binciken manyan laifuka (SCID) na rundunar Ƴan Sandan jihar Kano, inda ake gudanar da bincike.”

Wasu hotun da suka dinga zaga kafafen sada zumunta sun nuna yadda aka ga Aliyu Sani Madaki rike da wata bindiga a hannun a ya yin taron yaƙin neman zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP Rabi’u Musa Kwankwaso.

Average Rating

5 Star
0%
4 Star
0%
3 Star
0%
2 Star
0%
1 Star
0%

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *