Daga Mu’azu Abubakar Albarkawa, Kaduna
Majalisar Masarautan Zazzau karkashin Jagoranci Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, CFR ta bayar da umurnin Korar wani jami’intabMalam Sama’ila Abubakar Rimin Tsiwa, wanda ɗaya daga cikin Dogaran Fadar Zazzau daga aiki a Masarautanr.
A kori Dogarin ne bayan an zarge shi da yin lalata da wata matashi mai shirin yin aure bayan taje neman taimako gun sarkin Zazzau a fadar.
Wakilin Martaba FM a fadar ya ce “wata matashiya wanda take shirin Aure tazo Fadar Zazzau domin a sadata da Mai Martaba Sarkin Zazzau bisa neman taimako kan batun aurenta, ta gabatar da bayanan ta ga Malam Sama’ila wanda maimakon gabatar da ita zuwa inda ya kamata, sai ya yaudareta zuwa wani wuri dabam inda shi da abokansa suka yi lalata da ita.”
Zuwa yanzu dai Majalisan Masarautar Zazzau, ta umurci rundunan ƴan sanda da ta gaggauta kamalla bincike, kuma su gabatar da masu laifi cikin gaggawa a gaban Kotu domin yanke masu hukuncin dai-dai da laifinsu.
Haka kuma, Majalisan Masarautr Zazzaun ta dauki alkawarin bin sahun wannan batu domin tabbatar da an kwatarwa Matashiyar hakkinta.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ingantacciyar Maganin HIV (Ƙanjamau)
-
Muna Neman Tabarrukin Ku- Saƙon Gwamna Bala Ga Sarakuna
-
Hadimin Shugaba Buhari, Bashir Ahmad Na Fatan Yin Nasara A Kotu.
-
An Kama Ɓarawon Da Ke Tausaya Wa Talakawa A India.
-
Wata Kotu Ta Yankewa Wadume Mai Garkuwa Da Mutane Ɗaurin Shekara 7 Bayan Samunsa Da Laifin Satar Mutane.