Daga Suleman Ibrahim Modibbo.
Yayin da ƙasar Maroko ke bikin samun ƴancin kai, ma’aikatar shari’a ta kasar ta sanar da yi manoma tabar Wiwi kusan dubu 5 afuwa.
An samu manoman da laifin noma tabar Wiwi ba tare da wani izini ba daga hukumomi abin da kai ga tuhumar su.
An yi wa Manoman afuwa su sama da duba huɗu da 800 ne a jajibirin bikin ranar da Moroko ta samun ƴancin kai, in da Mai Alfarma Sarki Muhammad, na 6 ya dauki wannan mataki saboda dalilai na jinkai.
Wasu daga cikin Manoman dubu 4 da 831, tuni aka yanke musu hukuncin dauri a gidan yari bayan an tabbatar da laifukansu, yayin da ake gudanar da bincike a kan wasu, bisa dalilan cewa sun mallakin manyan filaye da ake gudanar da noman tabar wuiwui a cikinsu.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya