Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
Shugaban kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa tasirin yarjejeniyar musayar danyen mai da Naira wadda ta haifar da rage farashin mai a Najeriya.
Kamfanin ya sanar da hadin guiwa da MRS don sayar da fetur a gidajen sayar da mai na MRS a duk fadin Najeriya a kan N935 kan kowace lita.
Daily Nigerian ta rawaito, hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ta fito a shafukan sada zumunta na kamfanin a ranar Asabar, inda suka ce wannan hadin gwiwar na nufin tabbatar da cewa ragin farashin ya kai ga Al’umma kai tsaye.
Bankin Duniya ya ce har yanzu Najeriya ba ta kama hanyar yaƙi da rashawa ba.
Sojojin Nijar sun kashe Mahara 29 a Tillaberi.
idan za’a iya tunawa dai tun a ranar Alhamis din data gabata ne , matatar mai Dake sarrafa gangar mai 650,000 a kowace rana ta sanar da rage farashin zuwa N899.50 ga ‘yan kasuwa masu sha’awar saye, tare da bayar da bashi domin saukaka tsarin saye.
Wannan ci gaban dai ya haifar da fafutukar farashi a bangaren kasuwancin man fetur, inda kamfanin NNPC ya sanar da rage farashin zuwa N899 kan kowace lita.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.