Jami’an tsaro sun kaddamar da farautar Ƴanbindiga a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara, bayan harin da suka kai kauyen Banga, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu tare da sace wasu 26.
Wani mazaunin yankin, Ahmad Ɗan Baba Adamu, ya shaida wa Radio Nigeria cewa maharan sun shiga ƙauyen ne da misalin ƙarfe goma sha biyu na dare, in da suka fara harbe-harbe ta ko ina har zuwa ƙarfe ɗaya da minti Arba’in na dare ranar Laraba.
“Sun kashe wani mutum mai suna Ibrahim Kafinta da wata yarinya mai shekaru 18 mai suna Amina Mande. Sannan sun sace mata 14 da maza 12, wanda ya kai jimillar mutane 26,” in ji shi.
Wakilinmu ya ruwaito cewa rundunar sojoji da haɗin guiwar ‘yan sa kai sun rufe hanyoyin ficewar ‘yan bindigar a yankin Yamutsawa, tare taimakon dakarun sojin saman Najeriya. Duk da haka, har yanzu ba a cimma nasarar cafke su ba.
Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, DSP Yazid Abubakar, ya ci tura, domin bai amsa kiran wayarsa ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya