Lauyan kare haƙƙin bil’adama Femi Falana, ya yi gargaɗi kan kowane irin bincike da hukumomin tsaro za su gudanar kan yadda Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, ta samu damar halartar taron Kungiyar Majalisun Duniya (IPU) a birnin New York.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Babban Lauyan Najeriya ya ce binciken da hukumomin tsaro za su yi kan lamarin, zai iya jawo wa Najeriya abin kunya da raini maras amfani.
Jaridar PUNCH ta yanar gizo ta ruwaito cewa, Akpoti-Uduaghan ta yi jawabi a taron IPU a ranar 11 ga watan Maris, inda ta yi magana kan dakatar da ita daga majalisar dattawa bisa zargin rashin da’a.
Sanatar ta bayyana cewa an dakatar da ita ne domin a hana ta magana, kan zarge-zargen cin zarafin mata da tayi wa Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio.
A yayin wani zama na majalisar dattawa a ranar Talata, Akpabio ya mayar da martani yana mai cewa, halayen sanatar a taron IPU ya kunyata gwamnatin Najeriya da al’ummar ƙasar gaba ɗaya.
Rahotanni sun bayyana a ranar Lahadi cewa, Hukumar Tsaro ta farin kaya ta kasa (DSS) da Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), sun kaddamar da bincike kan yadda Sanatar Kogi ta samu damar halartar taron ba tare da an tura ta a hukumance ba.
Sai dai Falana yayi gargaɗi cewa, wannan bincike zai iya jawo wa wasu manyan jami’an gwamnatin Bola Tinubu abin kunya.
Bayanin ya ci gaba da cewa “A ƙarshe, abu ne da kowa ya sani cewa Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio, ya zargi Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da kunyata gwamnati da al’ummar Najeriya, ta hanyar kai karar dakatar da ita zuwa ga Kungiyar Majalisun Duniya (IPU).
“Akasin abin da Shugaban Majalisar Dattawa ke tunani, shi ne binciken da hukumomin tsaro za su yi game da tafiyar sanatar zai jefa Najeriya cikin abin kunya da raini maras amfani” Inji shi.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya