An faɗaɗa hanyoyin jigilar jama’a a birnin Riyadh don haɗa Diplomatic Quarter, inda yawancin jakadun ƙasashen waje ke da ofisoshin su.
Sabbin hanyoyin bas za su fara aiki daga King Saud University zuwa Diplomatic Quarter, kowace rana daga ƙarfe 6:30 na safe zuwa 12:00 na dare.
Ana iya duba cikakken jadawalin tafiyar a cikin manhajar Darb na jigilar jama’a.
Wannan faɗaɗawar na zuwa ne a matsayin wani yunkuri na Hukumar Masarautar Raya Birnin Riyadh, wajen inganta hanyoyin sufuri a birnin.
Bayan ƙaddamar da Riyadh Metro a watan Disamba na 2024, wanda ke da layukka shidda masu ratsa fiye da kilomita 176, hukumar na ci gaba da ƙarfafa hanyoyin bas.
A halin yanzu, birnin ya na da fiye da tashoshi da wuraren tsayawar bas 2,860, waɗanda ke hada jimillar kilomita 1,905, tare da ƙarfin ɗaukar mutum 500,000 a kowace rana.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya