Notice: Constant DISALLOW_FILE_EDIT already defined in /home/martabaf/public_html/wp-config.php on line 98
An ƙara faɗaɗa hanyoyin jigilar jama’a a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya. - Martaba FM An ƙara faɗaɗa hanyoyin jigilar jama’a a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya. - Martaba FM

An faɗaɗa hanyoyin jigilar jama’a a birnin Riyadh don haɗa Diplomatic Quarter, inda yawancin jakadun ƙasashen waje ke da ofisoshin su.

Sabbin hanyoyin bas za su fara aiki daga King Saud University zuwa Diplomatic Quarter, kowace rana daga ƙarfe 6:30 na safe zuwa 12:00 na dare.

Ana iya duba cikakken jadawalin tafiyar a cikin manhajar Darb na jigilar jama’a.

Wannan faɗaɗawar na zuwa ne a matsayin wani yunkuri na Hukumar Masarautar Raya Birnin Riyadh, wajen inganta hanyoyin sufuri a birnin.

Bayan ƙaddamar da Riyadh Metro a watan Disamba na 2024, wanda ke da layukka shidda masu ratsa fiye da kilomita 176, hukumar na ci gaba da ƙarfafa hanyoyin bas.

A halin yanzu, birnin ya na da fiye da tashoshi da wuraren tsayawar bas 2,860, waɗanda ke hada jimillar kilomita 1,905, tare da ƙarfin ɗaukar mutum 500,000 a kowace rana.

By Moddibo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *