Majalisar Dokokin jihar Rivers ta gabatar da sanarwar zargin aikata ba dai-dai ba ga Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyar sa Farfesa Ngozi Odu, wanda ke nuna fara aiwatar da shirin tsige su.
Sanarwar da aka samo daga majalisar a ranar Litinin, ta bayyana cewa ‘yan majalisar sun ce wannan mataki ya yi dai-dai da kundin tsarin mulkin Najeriya.
Sanarwar ta ce wannan mataki “yayi dai-dai da tanadin Sashe na 188 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 (wanda aka gyara) da sauran dokoki masu aiki.”
Sanarwar ta kara tabbatar da rade-radin cewa gwamnan na iya fuskantar tsigewa bayan hukuncin Kotun Koli, da ta amince da ‘yan majalisa 27 da ke biyayya ga tsohon gwamna Nyesom Wike, wanda ke takaddama da Fubara.
Wike wanda shi ne Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, ya kuma bayyana a makon da ya gabata yayin wata hira da manema labarai cewa, ya kamata a tsige Fubara idan an same shi da laifi.
“Siyasa ba wasa ba ce. Idan ya aikata abin da zai sa a tsige shi, to su tsige shi. Ba laifi ba ne,” in ji Wike.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya