Mutum hudu sun rasa rayukan su, yayin da wasu hudu suka jikkata bayan wani abu mai fashewa ya tashi, a ƙarƙashin wata motar haya a ƙaramar hukumar mulkin Biu ta jihar Borno.
Wannan fashewa ta faru ne a ranar Laraba 19 ga watan Maris, da misalin ƙarfe 2:30 na rana lokacin da wata mota kirar Golf 3 da Wakil Fari ke tukawa, ke kan hanyar ta daga Kimba zuwa garin Biu.
Bisa bayanan sirri da Zagazola Makama ta samu, wani ƙwararre kan yaƙi da ta’addanci a yankin Tafkin Chadi, ya ce bam din ya tashi ne a dai-dai lokacin da motar ta isa Sabon Gari a mahadar Kimba.
“Motar ta taka kan bam din ne lokacin da ta kai Sabon Garin, wanda hakan ya haddasa fashewa mai karfi,” kamar yadda rahoton ya bayyana.
Fashewar ta yi sanadin mutuwar fasinjoji hudu nan take, yayin da wasu hudu suka samu raunukka daban-daban. An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Babbar Asibitin Biu domin samun kulawar likitoci.
Jami’an lafiya a asibitin sun tabbatar da mutuwar waɗanda suka rasa rayukan su, sannan suka mika gawawwakin su ga iyalan su bayan ajiye su a dakin ajiye gawa.
Hukumomi na zargin cewa ‘yan ta’adda masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP ne suka dasa bama-baman, mai yiwuwa da nufin kai hari kan dakarun soja da ke aiki a yankin.
Bayan harin, jami’an tsaro sun kakkafa matakan tsaro a yankin tare da gudanar da bincike domin gano ko akwai wasu ƙarin bama-bamai da aka dasa, domin tabbatar da lafiyar masu amfani da hanya.
Haka kuma, hukumomin tsaro sun ƙaddamar da gangamin wayar da kai ga al’ummar yankin kan hatsarin da bam ɗin da bai tashi ba ke haifarwa, da kuma matakan kariya domin inganta tsaro.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya