Daga Zainab Adam Alaramma
Hukumar tace fina-fina da daf’i ta jihar Kano ta wanke Jarumar masana’antar Kannywood Maryam Yahaya bisa wani zargi da akai mata na rungumar wani saurayi a cikin wani bidiyo.
Abdullahi Sani Sulaiman, wanda shine Mai magana da yawun hukumar ne ya bayyana hakan ga freedom Radio
Ya ce, an kai musu korafi akan jaruma Maryam Yahaya kan wani bidiyo da ake yadawa a kafafen Sada Zumunta, Inda aka ga wani yana rungumar wata wacce ake zargin Maryam Yahaya ce, amma sun gudanar da bincike sun gano cewa ba Maryam Yahaya ba ce a cikin bidiyon.
Abdullahi Sani Sulaiman ya ƙara da cewa, shugaban hukumar tace fina-fina ta jihar kano Abba El-Mustapha ya baiwa daraktan dake kula da Yan masana’antar Kannywood damar gudanar da bincike don tabbatar da anyi adalci ga kowanne bangare.
Binciken dai ya wanke Maryam Yahaya saƙal, inda ya ce, bayan kammala binciken hukumar sun ta tabbatar da cewa Wacce ake zargin ba jaruma Maryam Yahaya ba ce, don haka suka ga dacewar su fito su shaidawa duniya cewa ba Maryam bace, saboda abun ya yadu da yawa bai dace su yi shuru akan maganar ba.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƴan bindiga Sun Sanya Harajin Miliyan 10 Ga Wasu Ƙauyuka A Jihar Katsina.
-
Soba Chairman-elect Molash sets agenda for the Council
-
Wani Babban Kwamandan Sojin Isra’ila Ya Baƙunci Lahira A Gaza.
-
Hukumar Lafiya Ta Duniya Ta Ayyana Ƙasar Masar A Matsayin Wadda Ta Kawar Da Sauro.
-
Ina nan daram kan takarar shugabancin ƙaramar hukumar Zariya – Hamisu Idris