April 18, 2025

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Kotun jihar Kwara ta tsare mutane biyar bisa zargin hallaka wata ɗaliba bayan sun yi mata fyaɗe suka sassarata.

Wata babban Kotun jihar Kwara, ƙarkashin mai shari’a Justice Hannah Ajayi ta tsare Abdulrahaman Bello da wasu mutane guda 4 da ake zargi da kashe wata ɗaliba mai suna Hafsoh Lawal a ranar 10 ga watan Febrairun wannan shekara da ke aji ƙarshe a Kolejin Ilimi da ke Ilorin a jihar ta Kwara .

Kotun ta sanya ranar 7 ga watan Mayun wannan shekarar domin fara sauraron ƙarar.

Dukkan wadan da ake zargin sun musanta zarge-zarge laifuka biyar da ake musu.

A cikin takardar tuhuma da aka gabatar gaban Kotu, Ana zargin Abdulrahaman ne da wasu mutane 4 da haɗa baki da kuma shirya kashe Hafsoh Lawal tare da sassara gangan jikinta.

Sannan ana zarginsu da haɗa kai wurin cire wasu sassa na jikinta , da kuma kwashe jinin jikinta, baya ga samunsu da wasu sassan jiki mutane da kuma jini.

Mutum na farko da ake zargin, mai suna Abdulrahaman Bello, a bangare guda ana zarginsa da yi gawar ɗalibar fyade , wanda haka ke kasancewa babbar da ke buƙatar ladabtar ga wanda ya aikata ƙarƙashin sashi na 283 na Penal Code CAP P4, na ɓangaren shari’a na jihar Kwara.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *