Wata babban Kotun jihar Kwara, ƙarkashin mai shari’a Justice Hannah Ajayi ta tsare Abdulrahaman Bello da wasu mutane guda 4 da ake zargi da kashe wata ɗaliba mai suna Hafsoh Lawal a ranar 10 ga watan Febrairun wannan shekara da ke aji ƙarshe a Kolejin Ilimi da ke Ilorin a jihar ta Kwara .
Kotun ta sanya ranar 7 ga watan Mayun wannan shekarar domin fara sauraron ƙarar.
Dukkan wadan da ake zargin sun musanta zarge-zarge laifuka biyar da ake musu.
A cikin takardar tuhuma da aka gabatar gaban Kotu, Ana zargin Abdulrahaman ne da wasu mutane 4 da haɗa baki da kuma shirya kashe Hafsoh Lawal tare da sassara gangan jikinta.
Sannan ana zarginsu da haɗa kai wurin cire wasu sassa na jikinta , da kuma kwashe jinin jikinta, baya ga samunsu da wasu sassan jiki mutane da kuma jini.
Mutum na farko da ake zargin, mai suna Abdulrahaman Bello, a bangare guda ana zarginsa da yi gawar ɗalibar fyade , wanda haka ke kasancewa babbar da ke buƙatar ladabtar ga wanda ya aikata ƙarƙashin sashi na 283 na Penal Code CAP P4, na ɓangaren shari’a na jihar Kwara.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya