January 17, 2025

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

“Kwararar masu aikata laifuka daga jihohin makwabta ne abin da ya taimaka wajen ƙalubalen tsaro”- Gwamnatin Gombe.

Daga Abdul’aziz Abdullahi

Majalisar tsaro ta jihar Gombe ta yi ganawar gaggawa domin shawo kan matsalar tsaro tsakanin makiyaya da manoma tare da masu satar Shanu da su ka addabi wasu yankunan jihar.

A yayin tattaunawar wadda mataimakin gwamnan jihar Manasseh Daniel Jatau, ya jagoranta ranar Litinin, majalisar ta sha alwashin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Gombe wacce ta kasance jiha mafi zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

Majalisar ta amince da ƙara tsaurara matakan tsaro domin kawo ƙarshen barazanar tsaron, sannan ta buƙaci al’umma da su sanya ido tare da kai koken duk wani motsin da ba su aminta da shi ba.

An yi arangama tsakanin makiyaya da manoma a jihar Gombe.

Ƴansandan jihar Gombe sun kama wasu matasa biyu bisa zargin fashi da makami.

Me ganawar Gwamnan Gombe da Shugaban NNPCL ta ƙunsa?

Gwamnatin ta kuma bayyana kwararar masu aikata laifuka daga jihohin makwabta a matsayin abin da ya taimaka wajen ƙalubalen tsaron.

Taron ya samu halartar SSG, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, kwamishinoni da abin ya shafa, shugabannin hukumomin tsaro, shugabannin ƙananan hukumomi da sarakunan gargajiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *