Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda (PSC), ta amince da karin girma ga kwamishinonin ‘yan sanda guda 20, da mataimakan kwamishinoni 19, da sufetoci 13, da kuma mataimakan sufeto 14.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin a Abuja, ta hannun shugaban sashen yada labarai da hulda da jama’a Mista Ikechukwu Ani.
Ani ya bayyana cewa an daga darajojin kwamishinonin yan sandan zuwa Mataimakan Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (AIG), mataimakan kwamishina zuwa kwamishina, SP zuwa CSP, sannan DSP zuwa SP.
Daga cikin kwamishinonin da aka daga zuwa AIG akwai Fasuba Olabode, Musibau Ajani, Aliyu Musa, Patrick Atayero, Gyogon Grimah, Olaiya Mobolaji, da kuma Chukwudi Ariekpere.
Sauran sun hada da Abubakar Aliyu, Olalolu Adegbite, Godwin Eze, Disu Olatunji, Alausa Tolani, Kareem Musa, Mohammed Dalijan, da Dan-Mamman Shawulu.
Haka kuma akwai Clement Robert, Musa Mohammed, Thomas Nabhoni, Abel Miri Zwalchir, da Ifeanyi Uka.
Daga cikin mataimakan kwamishina da aka daga zuwa kwamishina sun hada da Usman Tahir, Sunday Okoebor, Ayodeji Faniyan, Saka Ajao, Omole Ola, Hope Okafor, da Ajo Ordue.
Sauran su ne Olufunke Adeayo, Stephen Ogedengbe, Iyabode Agbaminoja, Adebowale Lawal, Ojo Adekimi, da Yemi Oyeniyi.
Har ila yau akwai Obasi Okereke, Moses Ottah, Felix Nnebue, Gazali Abdul-Salaam, Fidelis Ogarabe, da Olubode Ojajuni.
Ani ya bayyana cewa duk jami’an da aka daga girman su ciki har da SP 13 da DSP 14, sun gabatar da kansu a gaban hukumar, inda aka gudanar da jarabawa da tattaunawa kafin a basu karin girma.
Shugaban hukumar malam Hashimu Argungu ne ya jagoranci shirin karin girman, tare da goyon bayan sauran mambobin hukumar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya