Daga Mu’azu Abubakar Albarkawa
Kungiyar Direbobin Tankokin man fetur, PTD, reshen kungiyar ma’aikatan matatar man fetur da iskar gas ta Najeriya NUPENG, sun karyata rahoton cewa mambobinta na shirin gudanar da zanga-zanga.
Shugaban PTD na kasa, Augustine Egbon, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce mambobin kungiyar ba sa shirin yin kowace irin zanga-zanga.
Ya ja kunnen jama’a game da yadda wasu masu son zuciya da miyagu ke yi ruɗar su.
“Hakan ya haifar da firgici marar tushe da kuma hadari a cikin jerin hanyoyin rarraba albarkatun man fetur a kasar nan ta hanyar yada labaran karya da karya.
Mambobinmu ba sa shirin yin wata zanga-zanga kuma mun kuduri aniyar ci gaba da yi wa kasa hidima.
“Muna goyon bayan kokarin da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ke yi na dora tattalin arzikinmu kan turba mai kyau domin amfanin mu baki daya,”in ji shi.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya