Daga Suleman Ibrahim Modibbo da Firdausi Ibrahim Bakondi
Wasu rahotanni daga ƙasar Isra’ila na cewa, ƴan sanda sun kama wasu mutane 6 a lokacin da suke gudanar da wata zanga-zanga a kofar gidan Firayim Minista Benjamin Netanyahu da ke Caesarea a gabar tekun Isra’ila.
Masu zanga-zangar sun bukaci firaministan da yayi murabus, kan zargin da suke masa na gazawar da ta kai ga harin Hamas a ranar 7 ga watan Oktoban da ya gabata.
Rahoton ya bayyana cewa ana sa ran, nan gaba za a gudanar da wata gagarumar zanga-zanga a garin.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja
-
Fasinjojin wata mota huɗu sun riga mu gidan gaskiya wasu kuma sun jikkata a jihar Borno.
-
Yan Sandan Jihar Kaduna sun kama Ƴan Daba bisa zargin kai wa masu ibadar Sallar Tahajjud hari.
-
Kotun Ƙoli ta raba gardama kan rikicin Sakataren jam’iyyar PDP na tarayyar Najeriya.