Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) reshen jihar Benue, ta tabbatar da sace daya daga cikin jami’an ta mai suna Insfekta Nathaniel Kumashe.
Jami’ar hulda da jama’a ta hukumar Ngozi Ahula, ita ce ta tabbatar da sace shi a ranar Alhamis a Makurdi, babban birnin jihar.
Ahula ta bayyana cewa, jami’in wanda ke aiki a Wannue cikin karamar hukumar Tarka, an sace shi ne da misalin karfe 10 na dare a ranar Laraba.
A cewar ta, an sace jami’in ne a garin su da ke Tse Aboh Uchi-Mbakor, bayan dawowar sa daga taron tunawa da dan uwan sa da ya rasu.
Ta ce, ‘’Yan bindigar sun harba bindiga domin razanar da iyalan sa da makwabtan sa kafin su tafi da shi.”
Ana zargin cewa wadanda suka yi garkuwa da shi sun kai shi wata mabuyar su da ke wata karamar hukuma da ba a bayyana sunanta ba a jihar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya