Wasu mutane dauke da makamai da ake zargin makiyaya ne sun kashe manoma biyu, a hare-hare daban-daban da suka faru a wasu ƙauyukka da ke ƙaramar hukumar Gwer ta yamma a jihar Benue.
Wakilin mu ya tattara rahoto daga wata majiya a yankin, wadda ta nemi a ɓoye sunan ta cewa, makiyaya ne suka kashe waɗanda lamarin ya shafa a kan hanyar da ke kaiwa hedikwatar ƙaramar hukumar.
A cewar majoyar, “Ɗaya daga cikin waɗanda aka kashe an hallaka shi ne a ranar Laraba a ƙauyen Atukpu, kimanin kilomita ɗaya daga hedikwatar ƙaramar hukumar, yayin da aka kashe ɗaya a kan hanyar Naka-Adoka a wannan rana.
“Yanzu haka da nake magana da kai, makiyayan sun mamaye hanyar Makurdi-Naka, wadda yanzu babu kowa a kanta saboda tsoron harin, ” yana mai ƙarawa da cewa masu babura da ake kira ‘Okada’ ne suka gano gawarwakin waɗanda aka kashe.
Da aka tuntube shi shugaban ƙaramar hukumar Gwer ta yamma Victor Ormin, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa ɗaya daga cikin mutanen da aka kashe yana kan hanyar Taraku-Naka inda yake kokarin samo kayan rufin gidan sa.
Ya ce ɗaya kuma an kashe shi ne a yankin Adoka Naka, yana mai jaddada cewa kashe-kashen sun fara zama ruwan dare a yankin.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya