Jam’iyyar APC, ta musanta rade-radin da ke cewa akwai sabani tsakanin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa, Kashim Shettima, inda ta yi watsi da zancen cewa Tinubu na shirin sauya mataimakinsa gabanin zaben 2027.
Da ya ke zantawa da Daily Trust a jiya Alhamis , Daraktan Yada Labarai na APC, Alhaji Bala Ibrahim, ya ce wadannan rahotanni basu da tushe balle makama.
“Wannan jita-jita ce kawai maras tushe. Wadannan maganganu ne da bai kamata a dauke su da muhimmanci ba,” in ji shi.
“Ko da ace, a wani dalili, shugaba yana da niyyar sauya mataimakin sa, ba zai iya yin hakan shi kadai ba. Wajibi ne a tattauna da manyan jiga-jigan jam’iyya kafin daukar irin wannan mataki,” in ji Bala Ibrahim.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya