Daga Suleman Ibrahim Modibbo.
Kamfanin man fetur na Najeriya ya bayar da kwangilar gyara matatar man fetur da ta ke jihar Kaduna, wadda ake sa ran aikin zan kammala a watan Disamba na wannan shekara ta 2024.
DCL Hausa, mai yaɗa labarai ta internet ta rawaito, manajan daraktan matatar mai ta jihar Kaduna Dr. Mustafa Sugungun, ya ce, ana sa ran kammala gyaran da ake yi wa matatar ta Kaduna zuwa karshen shekararnan ta 2024.
Babban manajan wanda ya samu wakilcin manajan sashen ayyuka na matatar Mista Emmanuel Ajiboye, ya bayyana hakan a wajen ktaddamar da aikin gyaran wata makaranta da kamfanin ya yi, ya ce idan aka kammala gyaran matatar za ta samar da ayyukan yi, bunƙasa kasuwanci da ƙananan sana’o’i a yankin.
Tsadar Rayuwa: Ba Da Daɗewa Ba Abubuwa Za Su Yi Kyau -Gwamnatin Najeriya.
Hukumar EFCC ta ba wa jami’anta umarnin bincikar gwamnonin da ke kan mulki.
Me ganawar Gwamnan Gombe da Shugaban NNPCL ta ƙunsa?
Jaridar ta kuma rawaito an bayar da gyaran matatar ne a kan kuɗi Dala miliyan 741 ga wani kamfani na ƙasar Koriya ta Kudu mai suna Daewoo Engineering & Construction.
A halin yanzu dai yan Najeriya na ci gaba da shan mai da tsada tin bayan janye tallafin Man Fetur da gwamnatin Tinubu ta yi, masana harkar mai na cewa gyara matatar zai taimaka wajen rage wahalar da ake sha wajen siyen man fetur a wasu lokutan a Arewacin Najeriya.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya