Daga Suleman Ibrahim Modibbo
A wasu hare-hare da rundunar sojin saman Najeriya suka kaddamar sun kashe tarin ƴan ta’addda a Kaduna da Zamfara.
RFI ta rawaito, Daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin saman, Edward Gabkwet ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar jiya Lahadi a Abuja.
Mr Gabkwet ya ce rundunar musamman ta Operation Whirl Punch ta ci gaba da aikinta na gano sansanin ƴan ta’addda tare da tarwatsa su.
Ya ce bayanan sirri sun bayyana cewa ƴan ta’addan da ke addabar al’umma ta wajen kisa da yin garkuwa da su a ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar Neja su na zaune ne a jihar Kaduna.
Allah ya yi wa Sarkin Ningi Alhaji Yanusa Ɗanyaya rasuwa.
Iyalan Sarkin Kano Ado Sun Ƙaryata Alaƙa Da Zainab Wadda Take Iƙrarin Ita Ɗiyar Sarkin ce.
A cewarsa, karin bayanan sirri sun nuna cewa waɗannan ƴan ta’adda su na ƙaura daga dajin Allawa na jihar Neja zuwa dajin Malum na ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.
Nasarar sojin na zuwa ne yayin da bindiga ke ci gaba da cin karen su ba babbaka a jihohin Arewacin Najeriya, in da a makon da ya gabata suka kashe Sarki bayan sun yi garkuwa da shi.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja
-
Fasinjojin wata mota huɗu sun riga mu gidan gaskiya wasu kuma sun jikkata a jihar Borno.
-
Yan Sandan Jihar Kaduna sun kama Ƴan Daba bisa zargin kai wa masu ibadar Sallar Tahajjud hari.
-
Kotun Ƙoli ta raba gardama kan rikicin Sakataren jam’iyyar PDP na tarayyar Najeriya.