An samu tashin gobara a ofishin Ƴansanda na a karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano da sanyin safiyar ranar Litinin dinnan.
kwamishinan Ƴansandan jihar, Hussaini Gumel,ya bayyana haka ga manema labarai inda yace lamarin ya faru ne da misalin karfe 05:45 na safe inda wani gini ya kone gaba daya duk da cewa hukumar kashe gobara ta jihar ta kai dauki.
Gumel ya ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar har zuwa wannan lokaci.
Yace an killace yankin domin hana kutsawar bata-gari, domin akwai makamai da alburusai da ke cikin ofishin wannan dalilin yasa aka rufe shige da fice a wajen.
A halin yanzu dai babban jami’in Ƴansanda na yankin yana kan tantance wasu takardun da abin ya shafa kamar yadda kwamishinan ya fada.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Soba Chairman-elect Molash sets agenda for the Council
-
Wani Babban Kwamandan Sojin Isra’ila Ya Baƙunci Lahira A Gaza.
-
Hukumar Lafiya Ta Duniya Ta Ayyana Ƙasar Masar A Matsayin Wadda Ta Kawar Da Sauro.
-
Ina nan daram kan takarar shugabancin ƙaramar hukumar Zariya – Hamisu Idris
-
Za Mu Yi Ƙoƙarin Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana – NAHCON.