Daga Sani Ibrahim Maitaya
Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal, ya ƙaddamar da aikin ginin tashar mota ta zamani a Gusau babban birnin jihar.
Gwamnan ya ce sabuwar tashar za ta samar da dimbin ayukkan yi ga al’umma.
A ranar Litinin aka ƙaddamar da aikin gina tashar ta zamani, a kan titin Sokoto zuwa Zaria a Gusau.
Ƙungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jihar Zamfara.
Ƴan Bindiga Sun Halaka Askarawa 8 A Jihar Zamfara.
Sabuwar tashar za ta ƙunshi isassun wuraren ajiye motoci, da wuraren hutawa na direbobi, da ingantattun na’urorin tsaro, da tsarin bayar da tikitin shiga tashar.