Daga Fatima Sulaiman Shu’aibu
Tsohon Gwamnan jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido, ya caccaki Gwamnonin Arewacin Nijeriya da suka yi tafiya zuwa kasar Amurka taro kan tsaro, Lamido ya ce ziyarar tasu ta nuna rashin sanin makamar aikinsu.
A kwanakin baya ne, gwamnonin suka yi tattaki zuwa Amurka, inda suka halarci taron zaman lafiya da Cibiyar Zaman Lafiya ta Amurka ta shirya.
Da yake mayar da martani kan wannan kan zuwan nasu Amurka, a wani saƙo da Lamido, ya wallafa a shafin Facebook, ya ce tafiyar ta fallasa rashin gogewa da gwamnonin ke nunawa yayin da suke gudanar mulki.
Daga bisani Sule, yace idan da Gwamnonin sun yi tafiya zuwa Amurka don yin aiki kan yadda za a bunƙasa noma ko al’amurran kiwon lafiya ko wasu matsalolin gida da wannan zai iya zama mai amfani sosai ga al’umma.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
“Haɗakar da ake ƙirƙira da nufin ƙalubalantar Tinubu a 2027 za ta rushe nan ba da daɗewa ba”-Ganduje
-
Wike ya tabbatar da Fubara zai koma kujerar Gwamnan Rivers in ya nemi afuwa
-
Jam’iyyar SDP ta ce ba za ta shiga wata haɗaka ba a zaɓen 2027.
-
Ƙaramin Ministan Gidaje da Ci gaban Birane Yusuf Ata ya gargaɗi Kwankwaso kan batun jihar Rivers.
-
NNPP ta nesanta ta da Kwankwasiyya da su ƙungiyoyi ta na mai gargadin su dena bayyana kansu a matsayin cikakkun ƴaƴan jam’iyyar.