Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Babban Bankin Najeriya CBN, yace za a cigaba da amfani da kudaden naira kamar yadda yake bisa tsarin doka.
Express Radio ta rawaito cikin wata sanarwa da CBN ya fitar ta ce, ya lura akwai ƙarancin gilmawar takardar Naira a wasu daga cikin biranen kasar, wanda hakan yakan faru a harkokin cinikayya na yau da kullum.
CBN ya ƙara da cewa za a cigaba da karbar takardar naira bisa tsarin doka ta 2007, sashin na 20(5) inda ya ce yace babu wanda zai daina karbar kudaden Naira da CBN ya samar.
Sanarwar ta shawarci Jama’a da su ci gaba da amfani da takardun ntaira batare da jin wani ɗar ba.
A baya ne dai babbar kotun ƙolin ƙasar ta yanke hukunci kan cewa za a dena karɓar tsofaffi kuɗaɗen ƙasar a ƙarshen watan Disamba na shekarar 2023, bayan wata ƙara da wasu gwamnonin ƙasar suka shigar, inda suka nemi kotu ta hana CBN chanza kuɗin ƙasar da ya yi a lokacin, wanda hakan ya sa ƴan Najeriya cikin tasku.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Mutane 86 ne su ka yi ƙorafi a kan Shamsiyya -Yansanda.
-
Murna ta mamaye al’ummar Gaza byan cimma yarjejeniyar tsagaita ta dindindin.
-
Gwamnan Kano ya amince da murabus ɗin Kwamishinan Ma’aikatar Bibiya da tabbatar da Nagartar Aiki.
-
Gwamna Zulum zai saka tallafin man fetur ga manoman yankin da rikicin Boka Haram ya shafa.
-
Sarakunan da Fintiri ya naɗa bayan ƙirƙirar masarautu 7 a jihar Adamawa.