Daga Firdausi Ibrahim Bakwandi
Akalla mutane 10 ne aka kashe a tsakanin ranakun Asabar da Lahadi a hare-haren da aka kai a kan hanyar Ayilamo zuwa Anyin da kuma al’ummar Chembe da ke karamar hukumar Logo ta jihar Benue.
Daily Trust ta rawaito, da yake tabbatar da aukuwar lamarin kakakin ƙaramar hukumar Logo Paul Pevikya, ya ce, kisan ya zama ruwan dare gama gari, kuma yana bakin cikin bayyana cewa wasu makiyaya dauke da makamai sun kashe sama da mutane 10 a karshen mako da ya gabata.
An bayyana cewa daya daga cikin waɗanda abin ya shafa daliba ce a Jalingo na jihar Taraba wanda suka afka mata a daren ranar asabar din da ta gabata.
Dan uwan wanda abin ya faru da ita ya bayyana cewa, yaji lokacin da yar uwarsa take kiransa inda kafin ya isa inda take maharan sun kashe ta.
Manema labarai sunyi ta kokarin zanta da Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Benue , SP Catherine Anene, kan lamarin amma abu yaci tura.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƴansanda Sun Kama Wani Ɗan Kasar Aljeriya Da Bindigu A Zamfara.
-
Akwai Bindigogin AK47 Guda Dubu 60 A Sansanonin Ƴan Bindiga Ɗari 120 Cikin Jihohin Arewa Masu Yamma,-Rahoto.
-
Wani Babban Kwamandan Sojin Isra’ila Ya Baƙunci Lahira A Gaza.
-
An Sake Kama Wani Mutum Da Bindigogi A Yayin Da Trump Ke Yaƙin Neman Zaɓe.
-
Mutum Sama Da 20 Sun Mutu A Wani Harin Da Sojoji Su Ka Kai Kasuwa A Sudan.