Siyasa
Trending

Kotun Daukaka Ƙara Ta Bayar Da Umarnin Sake Zabe Wasu Ƙananan Hukumomin Jihar Zamfara.

Daga Firdausi Ibrahim Bakondi

Kotun daukaka kara da ke birnin Abuja ta soke zaben gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara.

Idan za’a iya tunawa a ranar 18 ga watan maris ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Lawal a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar ta Zamfara.

Sai dai kuma jam’iyyar APC ta kalubalanci nasarar Lawal, wanda ya tsaya takara a karkashin jam’iyyar PDP a gaban kotu sauraren kararrakin zaɓe a jihar, inda kotun ta amince da zaben Lawal, amma jam’iyar APC ta garzaya kotun ɗaukaka ƙara.

A ranar alhamis din da ta gabata ne kwamitin alkalai uku ya soke nasarar Lawal tare da bayar da umarnin sake gudanar da zaben a kananan hukumomi uku.

Daily Trust ta rawaito cewa, ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun hada da Maradun, Birnin Magaji da kuma Bukuyun.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button