Labarai
Trending

Gobara Ta Tashi A Ofishin Ƴansanda A Jihar Kano.

An samu tashin gobara a ofishin Ƴansanda na a karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano da sanyin safiyar ranar Litinin dinnan.

kwamishinan Ƴansandan jihar, Hussaini Gumel,ya bayyana haka ga manema labarai inda yace lamarin ya faru ne da misalin karfe 05:45 na safe inda wani gini ya kone gaba daya duk da cewa hukumar kashe gobara ta jihar ta kai dauki.

Gumel ya ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar har zuwa wannan lokaci.

Yace an killace yankin domin hana kutsawar bata-gari, domin akwai makamai da alburusai da ke cikin ofishin wannan dalilin yasa aka rufe shige da fice a wajen.

A halin yanzu dai babban jami’in Ƴansanda na yankin yana kan tantance wasu takardun da abin ya shafa kamar yadda kwamishinan ya fada.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button